Sunday, 6 August 2017

Yazeed ko Yaseer

[2/17, 1:08 PM] Ayshart one: Yazeed ko Yaseer
           Nah
Ayshart Farouq
           NWA

    
                35

Kuka Afnan ta shiga yi tana nuna Yaseer din da ya shigo Wanda shima kanshi mutuwar tsaye yayi yana kallonta sai dai sanin abunda ya aikata ne yasanya yayi tamkar bai taba ganin halittarta a duniya ba, ganin haka ya sanya Afnan tayo kanshi tare da ciyo kwalar shi, "wlh Allah shi yamin fede wlh shine Yazid kaci amanta ka cuce ni"
Buge hannuwanta yasir din yayi, " ke kinada hankali kuwa waye ke? Meye hadina dake da zakimin sharri?" Alh ya dube Yasir din yace, " ya isa haka yasir zo ka zauna abunda ta gama cewa Yazid kenan "
Jin haka ne ya sanya Afnan tayi wata uwar Kara tare da fashewa da wani matsananci kuka, cikin ranta tambayar kanta take,  me ke shirin faruwa Dani ne? meyasa Yazeed zai min haka? taya Yazeed ya koma Yaseer ? Gigitaccen Marin da aka dauketa da shi  ne ya dawo da ita cikin hayyacinta, sake daga hannu yayi ya sake dauketa da wani Marin Wanda saida taga wuta cikin tsananin fushi yake magana,
"Kin cuce mu Afnan, kin cuce kanki,  kin kuma cuce kauna da tarbiyar da mahaifinmu ya baki".
momy kam tunda ta zauna banda hawaye ba abunda takeyi, duniyar baki daya ta Mata zafi, mikewa tayi tana dubin su Yazeed din da suka zuba ma ikon Allah ido suna kallo,  " Dan Allah bayin Allah kuyi hakuri da Abunda ya faru" ta fada dakyar tana maida nunfashi, jin yanda take maganar ne ya sanya Ibrahim yayi saurin dubota amma kafin kace me daga kafarta keda wuya ta sulale ta fadi kasa, Ibrahim yayi kanta da sauri yana jijjigata,
Afnan da ke tasaye baki daya kasa komai tayi dakin kanshi duhu yake Mata wata irin juwa take gani ga wani irin matsanancin ciyon marar da ya taso Mata wata irin Kara ta kwala ta zube kasa yayin da jini yaketa bin kafafuwanta,

Ibrahim kam ya rude iya rudewa yarasa kanwa zaiyi ga mahaifiyar shi ga kanwar shi, duk da tsanar Afnan din da yake kasan cewar ita  taja komai, yasan tana bukatar taimako Ruwan da Yaseer yayi saurin kawowa ne yazubama momy amma Ina ko motsi batayi ganin haka yasan ya,
Ibrahim din cewa "pls Yazeed  Ku taimaka min mu kaisu asibiti Dan Allah."
Yazeed kam har zuwa lokacin haushin Afnan yakeji saboda tamishi abunda ba'a taba yi mishi ba.  Yaseer kuwa wani irin tausayinta ne ya kamashi sai dai ba yanda zaiyi don yasan ba yanda za ayi yace shi yamata ciki a zauna lfy.

Cikin motar Ibrahim aka sanya momy yayin da aka sa Afnan cikin mota Yaseer suka nuface asibiti,

Direct emergency aka nufa dasu don ceto rayuwarsu  bama kaman Afnan da taketa bleeding.

Cikin ikon Allah momy ta farfado sai dai jininta ya hau sosai don harma  yafi na dady hawa.
[3/19, 12:54 PM] Ayshart one: Yazeed ko Yaseer
              Nah
   Ayshart Farouq
             NWA

           36
Afnan kuwa har kusan magrib bata San inda kanta yake ba, cikin jikinta ma ya zube saboda wahala da damuwar da ta shiga  saida ma aka Kara Mata jini.

Har zuwa wannan lokacin kuma Yazeed da Yaseer suna nan a asibitin, shi Yazeed yana zaune ne kawai don amincin da ke tsakanin shi da Ibrahim,  Yaseer kuwa  Abubuwa da yawa suka sa shi zama a asibitin.
  Ibrahim ne yafito dakin da momy take, hannu yabasu sukayi musabuha tare da ce musu, " nagode kwarai fah da dawainiya Allah ya saka muku da alkhairi" suka karba da ameen,
Yaseer yace, " mushiga daga ciki munganta don wucewa zamuyi lokacin sallah na gabatowa,
Harararshi Yazeed yayi don shi bai so haka ba son yayyi su wuce tunda ga Ibrahim nan yazo, ba yanda zaiyi dole yabi bayansu suka shiga dakin da Afnan din take ciki,

Kwance take har zuwa lokacin, kallo daya zaka Mata kagane tana cikin mawuyacin hali saboda yanda take jan nunfashi da yanda take maida shi.

"Har yanzu bata falkla ba?" Cewar  Ibrahim yana duban nurse din da ke daura Mata drip a hannu,
"Gaskiya yanada wuya ta falka yanzu saboda Injections din da aka Mata masu karfi ne, inaga sai zuwa dare ko tana falkawa"

Cikin damuwa Ibrahim ya bude baki zaiyi magna, wayar hannnushi tayi kara, cikin ladabi yake karba wayar, Wanda ya nuna alamar da mahaifin shi yake magana, kallo daya zaka mishi ka tabbatar da baya cikin nutsuwar shi saboda yanda yaketa bawa mahaifin shi hakuri, jikinshi mace ya ajiye wayar.

Yazeed da Yaseer kuwa zuba mishi idanuwa sukayi ganin yanda yaketa gumi,
"What happen friend?" Yazee ya fada yana kallon shi,

Shafe zufan da ke  karyo mishi yayi, "their is problem friend I need you helps"

"Ok inajin ka how can we help u?"

Cikin damuwa Ibrahim ya ce, " dady yace yanzu yanzun nan inzo yana nemana kuma bayq so kafata ta sake takowa wajjen Afnan ya yafeta bata cikin 'ya'yan shi idan kuma na sake nayi bai yafe min ba",

" subhanallah" Yazeed ya furta, yayin da Yaseer ya fadi jagwab zaune kan gado yana dafe Kai,

" yanzu to ya zamuyi mu" Yazeed ya tambaya yana maijin haushin iyaye irin na Ibrahim da basu San kaddara ba.
Ibrahim ya ce, " Ina so Dan Allah Ku taimaka min ku Dan kulamin da ita, har zuwa lokacin da za'a sallameta nasan mahaifinmu ya fada ne kawai saboda fushin zuciya m sure kafin lokacin ya sauko daga fushin da yake da ita, pls friend don't say no",
[3/19, 1:40 PM] Ayshart one: Yazeed ko Yaseer
            Nah
  Ayshart Farouq
            NWA

           
              37
    Yaseer yayi saurin cewa "kada ka damu zamu taimaketa insha allahu", yafada yana kallon fuskar Yazeed da ta chanja kala,

Ibrahim ya ce, " thank you very much guys am really appreciate, zamuyi waya idan Ana bukatar wani abu"  ya fada yana basu hannu, yafita da sauri,

Cikin bacin rai Yazeed ya juyo ya dube Yaseer "me yasa kayi haka? Ko Kai kanada maccen da zata zauna ma da ita ne?"

Shima Yaseer fuskar shi tamke yayi magana" ko babu ni Zan zauna da ita,"

Tsaki Yazeed din yaja "wayasani ma ko Kaine kayi aika aikan"

Murmushi Yaseer yayi, " nagode Allah dai da kowa yasan waye tace ya Mata na tabbatar da ko yanxu ta buda baki zatace Yazeed ne ya Mata fede so nasan ko miyema Kai ne zaka hada mata cox at the first place Kai............."
"Just shout up crazy boy" Yazeed ya katse Yaseer cikin tsawa, idanuwan nan nashi sunyi jajur kallo daya zaka mishi kasan yana cikin bacin rai,

Tsaki Yaseer din yayi tare da fita kasancewar anfara kiraye kirayen magrib,

Bayan sallahr isha'i duka su biyu suna dakin ba Wanda yace da wani ci kanka kowa dannar wayar shi kawai yakeyi.

Nurse ce ta shigo dakin da sallamarta tana ce musu " yakamata fah mace tazo tayi jinyarta don akwai Abubuwan  da ake bukatar mace ta mata,"

Yaseer ya ce, "dole sai mace zatayi?,"
"No ba dole ba tunda ita kadai take a daki amma idan da mace zaifi, anyway ko mijinta ma zai iya, tunda dole mutum daya zai rika kwana da ita, Kai Doctor Yazeee kasan dokar ai,"
Gyada Mata kai kawai yayi,
tayi yana abubuwan da zatayi ta wuce.

" duk tsun tsun da yaja ruwa shi ruwa kan doka, ka daiji abunda nurse ta fada yanxu" inji Yazeed,

Tsaki Yaseer yayi " mai uwa a gindin murhu ba ya kukan ban koshi ba," wayar shi ya dauko ya Kira mahaifiyar shi cikin shagwaba da sakuwa yake magna,
" pls mom wlh yarinyar tana cikin mawuyacin hali, hava mom ko fadeela ce ki turo Dan Allah, oh my god yaushe fadeela ta tafi? Banji me ake cewa bangaren can ba amma ga alama bai samu nasarar convincing mahaifiyar tashiba ko da ganin yanda ya ajiye wayar,

Hada idanuwa sukayi da Yazeed " yadai zata zo ne?" Yazeed ya fada yana yamutsar fuska saboda baki daya asibitin ta gundure shi.

" bazata bar mijinta shi kadai ba" Yaseer ya bashi amsa

Yazeed ko Yaseer

[1/2, 10:42 PM] Ayshart one: Yazeed ko Yaseer
           Nah
   Ayshart Farouq

Nagarta Writers Association
   ©NWA©

           30
Kuka sosai Afnan keyi, yayin da Yazid yayi kwance reran yana maida nunfashi, ganin kukan nata bamai karewa ba ne yasanya yajawota jikinshi yana lallashinta,

" plz Afnan Dan Allah kiyi hakuri ki yafemin wlh bada son raina nayi miki haka ba,  i just don't know what to do, Ina cikin tsananin bukata ne shiyasa naga ke kadai ya dace ki taimaka min keda Zan aura believe me Afnan wlh ban taba aikata zina ba ya karashe maganar cikin kuka,

Tureshi tayi jikinta,
" bakada abunda zakace min in yarda da Kai Yazid, kuma kasani Alla yana ganin ka bazai taba barinka ba Allah ya isa tsakanina da Kai, ta fada tare da mikewa sai dai wani azbtacen ciyo taji Wanda yasanya ta sake komawa zaune tana fitarda hawaye.

Da sauri Yazid ya yunkuro don ya kamata sai dai cikin zafin nama ta bige mishi hannu,

" kada ka sake tabani macuci azzalumi, ka bude min kofa infita wlh ko inma abunda baka tsammani"
 
" Dan Allah Afnan kiyi hakuri ki gyara jikin ki sannan ki je plz Dan Allah ba Dan halina ba"

" Kai har kasan Allah ne? Ai ni bana tunanin kasan Allah don da kasan shi da bakayimun abunda kayimin ba, ka bude mun kofa infita nagaya maka," ta fada cikin tsawa,

Haka ya mike jikinshi duk a mace yaje ya bude Mata kofar,
Da kyar ta mike tana dingirshi hawaye nafita idanuwanta ta bar gidan tana jin dama ba a haifeta ba da ganin rana irin ta yau,

Keke napep ta samu tashiga ta isa gida, amma  kallo daya zaka Mata ka gane cewa ba lafiya ba,

Cikin faduwar gaba tana bin gini ta isa falon gidan, mahaifiyarta taci karo da ita zaune tana kallon sunnah tv,

" subhanallah Afnan lafiya kuwa? Me yake damunki ne?"

Kasa bata amsa Afnan din tayi sai kawai ta fashe da kuka,

Hankalin momy yayi matukar tashi   ta mike tsaye ta isa gurinta tana girgizata

"Ki fada min Afnan me yake damunki?, lahaula walakuwati illah billa, Afnan miye a zanenki haka?"

Jin wannan tambaryane ya sake jefa Afnan cikin rudani,
K'ank'ame momy tayi
" wayyo momy mutuwa zanyi marata ciyo takemin sosai "

Momy tayi ajiyar zuciya sannan ta ja diyar tata cikin tausayawa " kai wannan ciyon mara ya gwada miki bone Allah dai ya miki maganin shi, muje ciki ki wanke jikin ki kisha magani kinji"

Haka tajata takaita har daki tare da fitar Mata da magungunanta sannan ta fita tanata jimamen ciyon Mara irin na diyar tata,

Afnan kuwa ba abunda takeyi a toilet idan ba kuka ba,  rayuwarta ta Mata zafi ji take tamkar Allah ya dauki ranta ta mutu ta huta da wannan rayuwar duniyar,, ganin kuka bazai Mata magani ba yasanya ta daure ta gasa jikinta a ruwan zafi sannan tayi wanka ta fito,.
Pain relief ta samu ta Dan sha sannan ta kwanta cikin kankanen lokaci bacci ya dauketa Wanda ya kasance baccin bakin ciki mafi muni a rayuwarta.

Sai bayan la'asar ta falka, jikinta ba laifi taji sauki sosai sai abunda ba'a rasa ba, arwalla ta Doro  tayi sallah sannan ta sake kwantawa Sam bata damu da yunwar cikinta ba don tasan ko kadan bazata iya cin abinci ba,
Miss call din Yazid kan sunfi a kirga a wayarta tare da texts dinshi na ban hakuri amma ganin suma kara tunzarata yayi wata irin  tsanar shi takeji a cikin zuciiyarta, kashe wayar tayi baki daya sannan ta kwanta, sai gab da magrib ta tashi, momy ce ma ta matsa Mata tadan ci abinci,

           
              31

Saida Afnan ta share kwana da kwanakki tana ignoring call din Yazid duk da tasan ba karamin takura zuciyarta tayi ba, saida taga ta gasa shi da kyau sannan tafara daukan call dinshi, shima idan ta dauka duk  maganar da tazo bakinta gaya mishi takeyi sai daga baya   ya samu ya lallasheta da magangannu masu dadi har yasamu ya shawo kanta ta hakura  suka koma kaman yanda suke a da, amma  wani lokaci idan ta tuna abunda ya Mata takanji ta tsane shi da duk ma wani namiji a fadin duniyar nan ita dai fatan ta Allah ya tabbatar da auren su ko zata samu kwanciyar hankali.

Bayan sati uku da faruwar haka Afnan ta shiga tashin hankali na rashin ganin call din Yazid har na tsawon sati daya tun tana sharewa har abun yafara damunta kasancewar tun lokacin da ya Mata fyade tabar kiran shi sai dai shi ya kirata, ganin haka ne ya sanya ta yanke shawarar kiran shi taji ko lafiya sai dai yanzu kusan kwana biyu tana kiran wayar a kashe, hankalinta ba karamin tashi yayi ba gashi Abban ta yace,  iyayen yazid basu kirashi ba don haka ta gaya ma Yazid din jibi ya turo magabatan shi tunda ya dawo tun last week su kadai yake jira don yanada abunyi.

Kwance ta ke ta kudndunne cikin bargo kasancewar yau da zazzabi ta tashi da ciyon Kai ga wata irin kasala da takeji,

Momy ce ta turo dakin ta shigo da sallama,

" Afnan lafiyarki kuwa mahaifin ki na kiranki bakya dagawa,?"

"Rass rass! Gabanta ya fadi lafiya kalau momy kaina ne yake ciyo shiyasa nasanya  wayar silent  banji ba"

" eyya Allah ya sauwaka, tashi kije mahaifinki na neman ki sai kisha maganin" ta fada tare da wucewa

Haka Afnan ta mike jikinta duk ba dadi kanta tamkar ya cire saboda tsananin ciyo,

Falo ta same shi zaune kamar ko yaushe sallama tayi, tagaida shi tare da neman guri ta zauna,

Kallonta yayi cikin kulawa sannan yakira sunan ta da "Afnan"

"Na'am Abba" ta karba muryarta na rawa

Yaci gaba da cewa, "ina so ki san cewa duk abunda ya faru ga bawa daga Allah ne kuma Allah yana son bayinshi masu hakuri da tawakkali, Afnan yanzu Yaron da kike so ya kirani ya shaida min cewa ya fasa auren ki"

Wata irin Kara Afnan ta buga tare da faduwa kasa sumamma......

Har yanxu dai Ina Mai baku hakuri kan errors din da zaku gani manage ne kawai nake Ina typing din luv you all my fans

©Ayshart one©
[1/8, 9:53 PM] Ayshart one: Yazeed ko Yaseer
           Nah
Ayshart Farouq

Nagarta Writes Association
   ©NWA©

           32
   Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un Abba ya shiga fadi tare da kwalawa momy Kira, itama momy da sauri tashigo dakin, ganin Afnan kwance ya sanya ta rude ta shiga tambayar Abba " me yafaru da ita ne alhaji?"

Cikin dakakkiyar murya ya kwashe abunda yafaru ya gayamata, kuka momy tashiga rusawa tana fadin, "toh me tayiwa wannan yaron ne da zai saka Mata da haka? Gashi yanzu yaje ya kaimu ya baro",

Ganin kukan momy ba Mai karewa ba ne saima kara daga mishi da hankali da takeyi ne ya sanya ya rarume ruwa ya shiga zuba mata yana kiran sunanta.

  A hankali ta bude idanuwanta tar kan mahaifinta kanta ne takeji wani irin gingirim da shi, yunkurawa tayi zata tashi momy tayi saurin tayar da ita tana mata sannu, kallon mahaifiyar tata tayi idanuwanta cike da hawaye,
" momy kinji wai Yazid yafasa aure na"
Momy ta shafe Mata kwallar da ta zubo fuskarta " kiyi hakuri Afnan komai mukaddari ne, ko yanzu ma ai ba'a cire rai da tsammani tunda baki mishi komai ba"
  Gyada kanta tayi " momy Yazid ya cuce ni ya cuce rayuwata ya........... Bata ida fada ba taji zuciyarta ta hautsine wani irin amai ya taso mata, da gudu tayi toilet tamkar zata amaye yan hanjinta gashi dama cikin ba komai a cikin sa,

  Momy da ke bayanta sai sannu take mata cikin ranta tana matukar tausayin diyar tata da ta fada tarkon soyayya,

Tana kare aman momy ta rikota jikinta duk ya gashe yayi zafi sosai ba wanni karfi a tattare da ita,
Momy tace, " alhaji inaga fah ya kamata aje da ita asibiti a dubata don naga jikinta yayi zafi sosai kar wani Abu yazo ya sameta daga baya,"
Abba yace, " nima abunda nake tunani kenan, yanzu dai abunda za'ayi kije kibata abinci taci nama Ibrahim waya tun dazu zaizo ya dubata.

Haka momy taja Afnan ta kaita daki ta tsareta saida taga taci abinci amma abincin ko minti biyu masu kyau bai samu ba ta amayar da shi, hankalin momy ya tashi sosai, nasifa ta shiga yiwa yar tata don ita ganinta duk damuwar da tasawa kanta ne yasanya ta shiga wannan halin, saida taga hankalinta ya Dan kwanta sannan ta tashi tabar dakin,

Tana fita Afnan ta dora daga inda ta tsaya kuka ta shiga yi tamkar ranta zai fita, wata irin tsanar Yazid da soyayyar shi suka bijiro Mata lokaci daya, cikin ranta kuwa sai fadin takeyi, " Yazid ka cuceni ka rabani da mutunci na dama ashe ba sona kakeyi ba?, dama jikina kake so kuma ka samu Allah ya isa tsakanina da kai" haka taci gaba da kuka da surutai Kala kala ita kadai tamkar mahaukaciya, haka Ibrahim yazo ya sameta, shi kanshi ba karamin tausayi ta bashi ba allura ya Mata tare da wasu magungunna.

   Abba da momy kuwa haka suka sata gaba sunata kwantar Mata da hankali da magangannu masu dadi har takanji ta Dan fara samun relief din damuwarta.  

(Iyaye kenan Allah Kara mana son iyayen mu baki daya. Ameen)

Bayan kwana biyu da faruwar haka, ba wani chanji da aka samu kan rashin lafiyar Afnan saima abunda yayi gaba, zazzabi da amaye amaye kam ba'a ma magana abun ba karamin tayarda hankalin iyayenta yayi ba, shi yasa yau Abba ya yanke shawarar kiran likitansu don ya dubata yaga abunda ke damunta, tashin hankalin su daya kar ace ciyon zuciya ya kamata kan damuwar da ta sanya kanta a ciki.
            
         
              33
Kasancewar yau asabar dukan su suna falo Afnan da ba wani karfi a jikinta tana kwance ta dora kanta kan cinyar mahaifiyarta kallo daya zaka Mata ka gane tana cikin matsala saboda yanda ta Kara haske ta rame tayi fau da ita, yanzu haka ma aman tayi ga ciyon kan da yazame Mata tamkar kadangaren bakin tulu idanuwanta ma bata iya bude su sosai saboda azabar da takeji,

Doctor ne ya shigo da sallamar shi, bayan sun yi  'yan gaishe gaishe Abba ya bashi damar duba Afnan ba tare da bata lokaci ba yafara aikin shi.

Bayan ya kare yi Mata tambayoyi ne ya karbe fitsarinta,
Ya dube Abba " just give me five to ten minute I will be right back"  doctor ya fada tare da mikewa.

Batare ko da bata lokaci ba ya dawo duk suna nan zaune suna firar su,

Result din ya mikawa Abba, gwajin farko ya tabbatar da Afnan tana dauke da ciki na tsawon wata daya da kwana biyu.
Abunda idanuwan shi suka gani kenan mikewa tsaye yayi yana nuna likiti,
" amma dai likita wannan ba gaskiya ba ne ko?"
Doctor yace, "gaskiya alhaji abunda ka gani shine gaskiya 'yarka tana dauke da ciki"

" innalillahi wa'inna ilaihirraji'un Afnan kin cuce ne" Abba ya fada yana dafe zuciya saboda wani irin zafi da take mishi, ita kanta momy bata San lokacin da ta mike tsaye ba tana kalima, itama Afnan din mikewa tayi tana wani irin kuka Mai ban tausayi , yayin da Ibrahim da ke kokarin shigowa dakin yayi tsaye chak tamkar Wanda ruwa suka cinye,

Cikin tsananin tashin hanmali Abba yayo kan Afnan din yana "fadin kin cuce ni Afnan kin wargaza min tsari kin tuddamin mutunci na kin............" Bai ida fadi ba ya fadi kasa warwas saboda bugawar da zuciyar shi tayi lokaci daya,

Momy dake tsaye sai lokacin hawaye suka zubo mata, da gudu tayi kan Abba tana girgiza shi su Kansu su Ibrahim din kanshi sukayo suna salati,
Afnan ma cikin tashin hankali ta matsa kusa dashi tana fadin,  " wlh ba laifina ba ne fyade ya min wlh fyad........."

Marin da Ibrahim ya watsa  Mata ne ya sanya ta katse maganar,
" kika kashe mana uba wlh kema sai na kashe ki" ya fada cikin tashin hankali,

Doctor ya dube su "yanzu dai duk ba wannan ba mu dauki
Alhaji mu kaishi asibiti tunda nan ba kayan aiki"
Haka ko akayi aka kama shi akayi dashi asibiti cikin ikon Allah aka samu kanshi sai dai yana tashi ba abunda ya ce face " na yafeki Afnan har abada" wannan furucin ba karamin tayarwa momy da hankali yayi ba,

Afnan kuwa daga waje ta tsaya kasancewar an hanamata shiga dakin, sai rusar kuka takeyi tana cewa ba laifinta ba ne fyade ya Mata,

Sai da aka samu aka mawa Abba allurar bacci sannan Ibrahim ya dube momy yace,
" momy miye mafita yanzu akan Afnan don nasan Abba bazai taba barinta ta zauna mishi gida ba"

Momy ta dubeshi cikin damuwa tace,
" inaga tunda tace fyade ya mata kaman abun zaizo da sauki, yanzu kamata yayi aje a same yaron a gaya mishi idan ma ta Kama a shiga kotu shiga za'ayi don a fitar Mata da hakkinta"
Shawarar tama  Ibrahim dadi  shima,
waje ya sameta zaune rakube tana kuka
"Ke" ya Kira sunanta fuskar shi tamke,  "waye yamiki ciki? Kuma kikamin karya wlh yanka ki zanyi"
Saida ta fyace majina sannan tace,
"Yazid ne kuma wlh fyade ya min"
" kin san gidan su Yazid din?"
Gyada mishi Kai tayi,
" eh nasani"
"Ok tashi muje ki kaini ingan shi"

Batare da gaddama ba ta mike, momy tace,
Itama zata bisu sai Sagir ya tsaya gurin Abba don tafi son ayi komai a idonta, ba yanda Ibrahim baiyi ba don ta tsaya tace ita alan balan sai taje, ba yanda ya iya dole suka tasa Afnan gaba har gidan su Yazid din.
        
     
                  34
  A yanda Afnan keji ko daga bacci aka tadata zata iya zuwa gidan su don gidan bazai taba bace Mata ba har abada,

Hon sukayi maigadi ya bude musu suka shiga Ibrahim yayi parking duk suka fito,
Dai dai kofar da zata sada su da gidan suka bi wani mutum sukaci karo dashi, Wanda yanayin shigar shi ma zai tabbatar ma da shine mamallakin gidan,

Dakatar dasu yayi da  cewa, Ina zaku  masu gidan fah duk basa nan, hala bakuyi waya da hajiyar ba ne?"

Hannu Ibrahim ya bashi suka gaisa, yayin da momy ta gaidashi, ita kuwa Afnan kallo kawai tabishi da shi,
   Ibrahim ya dube shi yace, " Dan Allah ko Ina zamuga Yazid?"

" Yazid kuma? Ku kuwa me koke nema da Yazid?" Alhajin ya fada cikin mamaki,

Momy ta dube shi tace, "ko Kai ne mahaifin shi?"

Gyada musu Kai yayi " tabbas kuwa nine mahaifin shi wani Abu ne ya faru?"

Ibrahim yace, "kwarai kuwa wani Abu ya faru don kanwata tana dauke da cikin shi na tsawon wata daya"

" what?" Ya fada da karfi, cikin tashin hanakali " u most b mistaken, Yazid dina bazai taba ai kata wannan aikin ba, tun wurima kuje Ku nemo wanda yama yarku ciki amma ba Yazid ba"

Afnan ta fashe da koka " wallhi Allah shi yamin fyade Allah shine"

Jin maganar fyade da Afnan tayi ba karamin tashin hankali alhaji ya Kara shiga ciki ba,
Cikin mamaki ya sake kallon su " fyade fa ki kace?"

Afnana ta gyada Kai tana fyarce majina,

Saida yadan yi Jim na lokaci kadan sannan yace, " wannan magana bata yiyuwa anan Ku shigo daga ciki"  ya juya suka bi bayan shi,

Falon shi suka shiga suka zazzauna ya sake dubin Afnan " kin dai tabbatar da abunda kika fadi gskiya ne ko"

Sake gyada Kai tayi "eh"

Wayar shi ya dauko ya Kira Dan nashi, " kazo yanzu ina falo ina nemanka"

Cikin minti biyu yaron ya sauko daga sama cikin tafiyar shi ta kasaita hannuwanshi duka biyu suna cikin aljihun shi, sallama yayi ba tare da ya kalle mutanen da ke zaune ba, gurin mahaifin shi ya nufa " Abba gani kana nemana"

Cikin nutsuwa mahaifin nashi ya dube shi tare da nuna mishi Afnan "me yarinyar can ta maka ka Mata fyade?"

Yanda ya dube Afnan d'ai zai tabbatar maka da cewa Kalmar mahaifin nashi ba k'aramin ruda shi tayi ba,

Ita kanta Afnan din tana hada ido dashi taji wata irin mumunar faduwar gaba don ita bata taba gani  shi ba ma,

Haka Ibrahim ma da  yakasa b'oye mamakin shi ganin abokin aikin shi da yayi,

Cikin tashin hankali yace,
"Dad fyade fa kace? Ni fah ban ma taba ganin wannan yarinyar ba" ya fada yana kallon mahaifin nashi,

Ran Ibrahim da ya gama baci bai San lokacin da ya cakume wuyan shi ba yana cewa,
"Karya kake yi macuci, Yazid ka cuceni ka cuce zaman tare"

Shi kanshi Yazid din rayuwar shi ta gama baci, cikin tsananin fushi ya ture hannuwan Ibrahim daga wuyan shi, "dakata Ibrahim kada kayi da nasani daga baya wallahi tallahi ban taba ganin wannan yarinyar ba" ya fada yana nuna Afnan,

Afnan kuwa kuka ne yaci karfinta ita kanta tasan bata taba ganin shi ba toh amma me ke shirin faruwa da ita,
Cikin kuka tace, " ya Ibrahim ba shine yamin  fyade ba"

Baki daya kallonta sukeyi Ibrahim kuwa kanta yayi yafara jibgarta tamkar Wanda Allah ya aiko " don uban ki yau sai kin gayamin Wanda ya miki cikin nan"

Momy kam kuka kawai takeyi tana kiran " ku Kama min shi kada ya illata ta"

Baki dayansu kasa tare shi sukayi,
Afnan naganin zai kasheta ya sanya tace,
" wlh shi ne yamin yace idan nace shi yamin kashe ni zaiyi "
Jin abunda ta fada ne ya sanya Ibrahim ya saketa ya koma kan kujera yana dafe Kai saboda tsananin tashin hankalin da yake ciki,

Yazid kanshi cikin tashin hankali yace, " ni mukayi haka da ke?"

Gyada Kai tayi alamar eh.

Kafin kace, me tuni mahaifin shi ya kwashe shi da wani irin wawan Mari, " irin wannan tarbiya na baka? Wallahi Yazid ka cuce ni"

Afnan kuwa tsanani tausayin yaron ne ya kamata saboda tasan taci amanar shi ba kadan ba, sai dai dole ne yasanya tayi haka don ta ceci kanta,

Muryar da bazata taba mantawa a rayuwarta ba taji "wai dad hayaniyar me akeyi ne?"

Mikewa Afnan tayi tana nuna Mai maganar "wallahi wannan Yazid din ne yamin fyade"

Baki dayan su kallon shi sukayi, 

Cikin mamaki mahaifin nasu yace, " ikon Allah YASEER din ne kuma yanzu ya miki fyade? Toh me kike nufi? Su fah ba yan biyu ba ne kuma basa Kama da juna, Kai wannan yarinyar Sam bakida  gaskiya kawai ki fadi tsakani da Allah Wa ya miki fyade  a cikin su yazeed ko Yaseer?,?

Ni dai marubuciyar nace daya daga cikin su ne ya Mata fyade, toh waye daga ciki YAZEED KO YASEER?

Masu karatu Ku biyoni next post don jin waye yazeed da Yaseer kuma Wa yamata fyade a cikin su

©Ayshart one©

Sunday, 19 March 2017

Yazeed ko yaseer

AM] Ayshart one: Yazeed ko
Yaseer
Nah
Ayshart Farouq
Nagarta Writes Association
©NWA©
.
25
Guri ta samu ta zauna tare da cewa, " Abba Ina
wuni, gani ance kana nemana"
" lafiya kalau Afnan" ya karba yana kallon ta cikin
fari'a da kulawa irin ta da da mahaifi,
Ci gaba yayi da magana yana kallon Ibrahim da
Sagir, "dama ba komai yasanya nataraku anan na
ga face Ku zamo shaida a gare ni akan Afnan a
matsayinku na yayunta"
Gaban Afnan yayi matukar faduwa toh me
Abbanta ke nufi ne? Tsura mishi ido tayi cikin
tsanani tashin hankali don jin me zai fada,
Wannan Karon baki daya annaurin fuskar shi ya
chanja lokacin da yake magana, "Alhamdulillahi
nasan nabaku tarbiya gwargwadon ikona
musamman ma ke Afnan, saboda babu wani Dare
da zan runtsa face nayi tunani matsayin hakkin ki
da yarataya a kaina, wani lokaci banma sanin
lokacin da hawaye suke zubo min idan na tuna
cewa ke diya mace ce tarbiyantar dake yanada
matukar wahala saboda idan kika lalace toh duka
al'umma sun lalace haka kuma idan kika gyarau
duka al'umma sun gyaru, hakika ban fahimce
abunda nake miki na shiga hakkin ki ba sai jiya
da mahaifiyar ki take Kara tuna min, ban kara
gane maganar ta tayi tasiri a kaina ba saida naji
kina waya jiya misalin karfe biyu na dare"
Wannan karon Afnan fashewa tayi da kuka tana
kallon mahaifinta, cikin ranta kuwa sai cewa ta
keyi, " nashiga uku ni Afnan yanxu duk Abba yaji
maganar da muke jiya,
Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un" ta fadab tuna firar
da sukayi jiya duka akan aure ne tana bawa
Yazeed hakuri akan cewa suma iyayen su biyayya
suyi abunda suke so ita kanta tana bukatar
auren,.....
Katse Mata tunani yayi da cewa,
"hakika sai jiya na tabbatar da cewa aure shine
mutuncin duk wata diya macce da take rayuwa a
doron kasar nan, tabbas Afnan na tauye miki inci,
na shiga rayuwarki da yawa na hanaki walwala
da sukuni akan kawai ingina rayuwarki don
zamowa Mai dogaro da Kai Ashe ban sani ba
kara ruguza miki rayuwa nayi, ta hanyar tsananin
da nake miki gashi kin koyi yin karya karatun ma
da nakeso kiyi shi kanshi yanzun bayi kikeyi ba
soyaya kikiye right ?" Yafada yana kallonta,
Girgiza mishi Kai tashigayi "a'a Abba Dan Allah
kayi hakuri kamini rai wlh Allah bazan karaba
Abba wayar tawama ka karbe duk wani Abu
dazakayi min kamin amma Dan Allah abbana
kada kayi fushi dani, ka hukunta ni ta ko wace
hanya amma Abba kada ka hukuntani ta hanyar
yin fushi Dani" kuka ta fashe dashi Mai tsanani,
Mikewa mahaifin nata yayi tare da komawa kusa
da ita yajawota jikin shi,
" yi shiru Afnan bakimin laifin Komai ba facema
birgeni da kikayi da kika nuna biyayya ma
iyayenki yafi komai muhimmanci a gurin ki dukda
cewa wani guri ki kaucewa iyayen naki amma duk
da haka ni nafi kowa laifi akan abunda kika
aikata na saving number namiji da sunan mace,"
Juyawa yayi tare da kallon momy da dasu
Ibrahim " Ku zama shaidata ni Usman nabaiwa
Afnan damar
ta gayawa wanda takeso ya turomin magabatan
shi"
Wata irin dagowa tayi tana kallon mahaifinta,
Duk da cewa maganar tamata dadi amma ita
harga Allah ba haka taso ba,
Gyada mata Kai yayi am serious Afnan kice mishi
ya turo min magabatan shi, Ina so infita hakkin
ki ne, inaso inaga magabatan shi shi zai sanya in
yadda da gaske yakeyi koda kuwa ba da wuri
za'ayi auren ba idan da wuri za'ayi ma walillahil
hamdu a shirye muke",
Kunya ta Kama Afnan "a'a Abba ni nafasa
karatuna zanyi"
" kaji ja'irar yarinya karatun ma da kika jama
baya taya zakiyi karatu ai idan muka barki zamu
tabka babban kuskure a rayuwar mu gashi tun
yanzu anfara haka ina gaba" inji momy
Abba yace, " a'a zainab ko gaba bama ganin
komai da yardar Allah,
Afnan ai aure baya hana boko hakama boko baya
hana aure kaman yanda mahaifiyar ki ta
gayamin,
Idan har minjin ki ya baki damar kici gaba da
karatu walillahil hamdu idan ma hanaki ci gaba
yayi duk daya ne Allah dai yamana jagora a
rayjwarmu kawai,"
Dukan su suka karba da "Amin"
26
Afnan kam har kaguwa tayi Abba ya sallameta
taje ta fadawa Yazid dinta wannan good news
din,
Kaman Abba yashiga ranta " toh uwata aje a
gayawa surikin nawa Ko"
Kunya ta kamata "uhm ni fah Abba na fasa"
Ibrahim dake zaune ya galla Mata harara " ai
haka zakice ki rika mawa momy karya kina satar
hanya kuna haduwa"
" ya subhanallah wai me suke nufi ne? Ba dai duk
abunda take suna hankalce da ita ba?"
Kukan shagwaba tasanya " Abba ka ganshi ko?"
" kyaleshi uwata shima na bashi nan da sati biyu
yafadi yarinyar da yake so aje amishi magana"
" zaro idanuwa yayi yana sosa keya, "uuhm dama
wlh Abba Ina so muyi magana da Kai kan wata
yarinya amma ban San ta inda Zan Fara ba,"
Dariya akayi duka momy tace, " yanzu ai
kanwarku ta buda muku ta inda zaku Fara don ko
sagir nasan can akayi"
Sagir yace, " tab momy rufa min asiri ni ai har
yanzu yaro ne ga dai su big bros nan masu
shema'u da Hafsa"
Harara Ibrahim ya watsa mishi " Ina wasa da kai
ne?"
Dady yayi murmushi yace, " kasameni anjima
muyi maganar" ya fada tare da mikewa,
Momy ma mikewa tayi tabi bayan shi,
Afnan dai kasa mikewa tayi don gudun tsokanar
Sagir don tasan tana mikewa zai hauta da
tsokna,
Ibrahim ya harareta "toh ai sai ki tshi ko kinxo
kin muna zaune kina kinibibi"
Zunburo baki tayi tare da mikewa dama abunda
take so kenan,
Dariya suka hauta da ita don tune sun ganota,
bata kulasu ba ta wuce abunta tana murna,
Tana shiga daki kan gado ta fada tare da kiran
Yazid,
Bugu daya ya dauka tamkar dama jiraye yake da
ita,
" albishirinka habibina" yanda tayi maganar saida
ya lumshe ido saboda dadin muryarta,
" goro" yafada a kasalance, " amma Allah yasa
bani ke akayi"
Dariya tayi,
" Kai wani lokaci haka kake tamkar aljani,"
Mikewa yayi daga kwancen da yake don jin me
zata fada,
" Ina jin ki plz na kagara inji"
Dariya tayi tare da kwashe duk yanda sukayi da
abbanta ta gaya mishi,
Yanda yaji maganar yana tunanin a duniya ba
Wanda yakaishi jin dadi " Afnan da gaske kikeyi
kuwa ko tsokana na kikeyi" ya fada cikin tsantsar
farin ciki,
" Allah da gaske nakeyi Yazid Abba yace ka turo
magabatan ka"
"Alhamdulillahi Afnan nayi farin cikin jin wannan
maganar taki sosai insha allahu nan da 1 wk
zasuzo amma kafin hakanan yau zanzo zance
gidanku nasan dai ba matsala ko?" Ya fada
tamkar yayi tsale yaganshi gurinta,
" Zan sanarda Abba duk yanda yace sai in sanar
dakai duk da bana tunanin zai hana,"
" toh ba damuwa sai naji ki".
Haka dai sukata waya suna jin su tamkar sunfi
kowa farin ciki a fadin duniyar nan,
Bama kaman Yazid da yake ganin yakusa cimma
burin shi kan Afnan don yana ganin wannan
hanyar ce kadai zaibi don ganin yasamu abunda
yake so a gurinta.
Dan Allah masu karatun wanna novel kuyi hakuri
da yanda kuka samu typing din nasan dole a
samu kura kurai da yawa a ciki kasancewar
wayata tanada matsala don mota ta takata
wannan ma da kyar nayi shi saboda sizing din da
wayar keyi.
Nagode
©Ayshart one©
[12/29/2016, 8:36 AM] Ayshart one: Yazeed ko
Yaseer
Nah
Ayshart Farouq
Nagarta Writers Association
©NAW©
27
Haka Afnan taje ta sanar da mahaifinta yanda
sukayi da Yazid din,
Yaji dadi sosai har yabashi damar yazo amma
yau ka dai don shi baya son yawan firan nan ba
tare da anyi tsayayar magana ba,
Haka taje ta sanar da Yazid, yayi murna sosai da
jin maganar ta ai kuwa 8:00 ya isa gidan su.
Lokacin Afnan taci kwalliya tamkar wadda zataje
gasar kyau, falon baki ta kaishi yayin da ta hada
mishi kayan motsa baki iri iri,
Lokacin da ta shigo falon suma ne kawai baiyi ba
gurin kallonta, don baki daya ta tafi da tunanin
shi da hankalin shi har baima San lokacin da
mike yaje gabanta ba.
Ganin haka ne yasanya tayi tsaye cak tana kallon
shi don ganin abunda yake shirin aikatawa,
Ai kuwa kafin kace mi tuni ya rungumota yana
shin shinar kamshinta duk ilahirin jikinshi rawa
yake idanuwan shi sunyi jajur tamkar
mayunwacin maye,
Cikin tsananin tashin hanakali ta tureshi daga
jikinta,
Cikin tsawa take magana, " meye haka ne Yazid?
Me yasa kai sam baka tsoron aikata abunda Allah
yayi hani dashi? nifa ba matarka ba ce meyasa
kake son tabamin jiki?,"
Dafe kanshi yayi da hannayen shi duka biyu, " oh
my God! Me nake shirin yi ne?, Afnan am totally
out of my control wlh jina nake yau tamkar
ankawo min ke a matsayin matata plz Dan Allah
kiyi hakuri wlh shaidan ne ya rudeni plz Afnan,"
Yanda yayi maganar tamkar yayi kuka,
Abunka da so nan take tausayin shi ya kamata,
Hararan shi tayi, " toh naji amma kaji kasake min
irin haka Dan Allah"
" insha allahu bazan sake ba" ya fada yana sosa
keya, " but plz kimin alfarma in rika hannunki in
kaiki ki zauna" ya fada cikin sigar zolaye harda
kanne ido,
Dariya tayi tare da wucewa "idan zaka zo ka
zauna ka zo idan bazaka zo ba ga hanya nan
Allah raka taki gona,"
Shima cikin dariyar yazo ya zauna kusa da ita
yana kallon ta "wai kin ganki? Allah tamkar
amarya"
" uhhm! Allah ko?"
Gyada Mata Kai yayi "sosai kuwa my Afnan"
Agogon hannunta ta duba "kaga fah lokaci na
wucewa gashi bakama ci komai ba" ta fada tare
da Fara zuba mishi abincin,
Haka yaci abincin dukda bayaji yunwa, yasan
idan yace bazaici ba rigima kawai zasuyi,
Fira suka shigayi sosai tamkar ranar suk Saba
haduwa,
Bashi yabar gidan ba sai kusan 10:30 shima ba
don yaso ba sai dai don ba yanda zaiyi ne.
Yau sati biyu da faruwar haka amma ba Yazid ba
samatar sa, hankalin Afnan yayi matukar tashi
gashi ko ta Kira wayar shi bata zuwa,
Kwance take kan gado idanuwanta na kallon
sama hawayene keta sintiri a fuskarta, tunani da
yawa a zuciyarta " toh me yasame Yazid ne?, ko
kuwa dama bayada ra'ayin aurena ne?, Kai
wannan bazaima yuyuba Yazid yana sona nasan
bazaimin haka ba"
Wata zuciya tace, " kika sani ko matsala ya samu
daga iyayen shi ne" wata zuciyar kuwa cewa tayi,
kila kuwa wani Abu ya sameshi Kai kilama
mutuwa yayyi baki sani ba.
Ai kuwa tamkar wani ne ya gayamata, ta shiga
rera kuka tamkar ranta zai fita,
Wayarta ce tayi ringing da sauri ta mika hannu ta
dauko tana addu'ar Allah yasa Yazid dinta ne,
Sai dai kash! Ba Yazid idanuwanta suka gani ba
sunana mahaifinta ta gani, ai kuwa lokaci daya
hankalinta ya sake matukar tashi don tasan
wannan kiran bama na lafiya ne ba,
Cikin muryarta da ta dusashe ta dauki wayar,
Sallama kawai mahaifin Nata ya karba tare da
cewa, " uwata kizo Ina neman ki yanzunnan" bai
tsaya yaji Mai zatace ba kawai ya kashe wayar,
28
Wayar Afnan ta tsurawa ido " toh me ke shirin
faruwa ne? Dole ne ma nasan maganar Yazid
abba zaimin toh me zance masa?"
Ganin batada mahita ne yasanya ta mike taje ta
wanke fuskarta sannan ta nufe gurin kiran da
Abban nata ke Mata.
Da sallama ta shiga dakin mahaifin nata, bayan
ta gaidashi ya karba cikin fari'ar shi, yamata izini
da ta zauna, bayan ta zauna ya dubeta " me yake
damun ki ne naga idanuwanki sunyi ja,"
Murmushi ta kakalo "ba komai Abba daga bacci
na tashi,"
" eyya ai kuwa da nasan bacci kike da ban takura
miki ba"
" a'a wlh Abba ai ba komai dama lokacin tashina
yayi ai"
Yace, " OK dama na kiraki ne kan maganar yaron
da kika ce kina so,"
Ras! Gabanta ya fadi
Yaci gaba da magana, " naji dadi sosai kan
abunda yaron yayi don haka da yayi shi zai nuna
yaron kirki ne kuma da gaske yakeyi don kusan
kwana biyu kullun sai ya kirani ya gaidani, yanzu
haka ma bamu dade da kare waya dashi ba shida
mahaifin shi,
Ya bani hakuri kan cewa basu samun zuwa
wannan satin sai bayan sati biyu saboda
ankwantar da Yazid din bashida lafiya kuma wai
zaiyi tafiya a wannan satin sai dai yadawo,"
Gaban Afnan ya fadi hankalinta yayi matukar
tashi, duk da kwarai taji dadin maganar da
mahaifin nata yayi amma jin rashin lafiyar Yazid
sai taji duk ta kara rikicewa,
Abba yaci gaba da magana "yanzu dai nace masu
suyi hakuri nan da sati biyu masu zuwa sai ayi
maganar saboda nima tafiya zanyi a yau kuma
ina tunanin zanyi sati biyu ban dawo ba shi yasa
na kiraki ingaya maki don infitar miki da hakkinki
dukda nasan wannan maganar ba dole ne sai
kinjita ba amma abun ne yayi matukar birgeni na
ganin mutanen sun San hakkin Dan Adam sosai.
Afnan tayi murmushin jin dadi, " adawo lafiya
Abba Allah ya tsare yakai lafiya"
"Ameen" ya fada tare da cewa, "amma fah uwata
baki kyauta ba da baki gayamin surukin nawa ba
lafiya ba"
Rufe idanuwanta tayi "ai Abba yaji sauki"
" toh Allah bida lafiya" yafada tare da mikewa,
" ki kiramin momyn ki lokacin tafiyata na
matsowa,
"Toh abba" ta fada tare da mikewa.
KaromKaroma taci da momyn zata shiga falon
shi yasa bata gaya Mata ba ta wuce kawai
dakinta ta fada kan gado tana hamdala.
Number Yazid ta sake dialing amma still number
bata zuwa, tsaki tayi tare da wulgar da wayar,
Hakika tasan tana muradin jin muryar shi tare da
marmarin ganin kyakkyawar fuskar shi.
Safiyar yau ma haka ta tashi da mafalkan Yazid
iri iri, ji take yau bata iya rayuwa idan bata ganshi
ba ko taji muryar shi ba, haka ta shirya taje
makaranta jikinta duk ba dadi
Bayan sun kare lectures ne sun fito tana zaune
kan wata kujera tana Danna wayarta taji anmata
sallama,
Amsawa tayi ba tare da ta dago fufuskarta ba jin
ya Kira sunana ta da Afnan ne yasanya tayi
saurin dago fuskarta,
29
Karaf suka hada ido da Yusuf abokin Yazid,
Murmushi tayi tere da cewa,
" a'ah manya gari kwana biyu ka buya kaida
abokin ka ya jikinshi?"
Murmushi yayi shima, " Alhamdulillahi he's
getting better amma fah fushi ya keyi da ke,"
Zaro idanuwa tayi "fushi fah kace?, "
" eh mana, ace yanzu duk rashin lafiyar da Yazid
yayi kikasa zuwa dubasa gashi kullu cikin kiran
sunan ki yake duka gidansu ba Wanda bai sanki
ba har su Kansu sunyi mamakin rashin zuwanki
asibiti duba shi,"
Jin an ambace asibiti yasanya tayi saurin dagowa
ta dube Amnu, asibiti fah kace? shi Yazid din ne
ya kwanta asibiti?
" uhum sosai kuwa yanzu haka ma yana can"
Idanuwanta cike da kwalla, "Allah ni ban san ma
bashida lafiya ba sai jiya don kona Kira wayar shi
bata zuwa"
Aminu ya dubeta cikin tausayawa " gaskiya Yazid
bai kyauta ba amma yanzu ya kamata kije ki
dubasa tunda kinji "
" wane asibiti aka kwantar dashi?"
Ya gayamata sunan asibitin yayi,
Duban shi tayi cikin damuwa " kash gashi
nasarawa hospital ba a shiga yanzu sai 4"
" gskiya kam ba a shiga amma idan yanzu zakije
muje in ajiyeki don Ina cikin masu jinyar shi za'a
barni nashiga dake"
Ganin wannan ce kadai damar da zata iya zuwa
dubashi ya sanya ta amince,
Cikin farin ciki aminu ya dauketa a motar shi
suka nuface asibiti,
Suna isa likaita ya tabbatar musu da an
sallameshi yanzunnan,
Haka suka fito jikin Afnan duk yayi sanyi gskiya
tana son ganin Yazid,
Ameenu ya dubeta " yakamata gsky kije gidansu
ki dubashi"
"A'a gaskiya bazan je gidansu bah idan naje mi
zance?"
Murmushi yayi " ai ba kya isko mum dinshi sai
daiko kannen sa"
Afnan bata so zuwaba amma aminu yata yimata
dadin baki har ta amince da maganar shi ta bishi
gidansu Yazid,
Kallo daya zaka Mata ka gane cewa bata cikin
nutsuwarta, har suka isa gidan ita dai bite kawai
take da shi gidan
Gidan ba Kara min kyau yayi Mata ba, cikin ranta
tace, " gske dai Yazid yake Dan gata"
Batare da fata lokaci ba aminu ya kaita dakin
Yazid din, nuni yamata da ta zauna, zama kawai
tayi amma duk ilahirin jikinta rawa yake,
Yazid ne yafito daga wata kofa tamkar wand bai
taba ciyoba don har kiba yadan Kara,
Wanni kallo sukayiwa junan su shida Aminu, take
aminu yabi ta kofar da yazid din yafito yafita
yana Dan murmhshi,
Ganin haka ne yasanya hankalin Afnan yakara
tashi,
Cikin fari'a Yazid ya karaso yana cewa,
" wow Ashe dai kinyi missing Dina da yawa my
princess"
Wani kallo tayi mishi cikin tuhuma, " me kake nufi
Yazid ba dai lafiyarka kalau ba"
Murmushi yayi tare da zama kusa da ita tamkar
ya shiga jikinta,
",dama gwadaki kawai nayi don Inga irin son da
kikemin"
Mikewa tayi, " miye haka Yazid? Kada kasake min
irin wannan wasar bana so?"
" oh common baby" ya fada tare da fizgota ta
fado jikin shi "am sorry plz baby na wlh nayi
missing dinki,
Yanda yake maganar yayi matukar bata tsoro don
haka ta ganshi tamkar ba Yazid dinta ba
idanuwan shi sunyi jajur,
" don girman Allah ka sakeni in wuce gida jirana
akeyi"
"Nasani mana amma ai bazakije haka ba bakisha
ko ruwa ba"
" uuhm a'a ni nagode"
" murmushi yayi tare da sakinta ya mike yayi
gurin fridge, tana ganin hakanan tayi wuf zata
fita sai dai kash an rufe kofar ta baya,
Tana ganin haka ta fashe da kuka,
" na shiga uku ni Afnan don girman Allah Yazid ka
budemin kofarnan infita,
Bai kulata ba sai murmushin ketar da yakeyi, molt
ta dauko ya nufota,
"Sai kinsha ruwa zan bude miki kifita " ya fada
yana mika Mata molt din,
Da sauri ta amsa ta Dan kurba,
" toh gashi nasha muje"
" naki wayon" ya fada tare da amsar molt din ya
shiga dura Mata ita saida yga ta shanye kaf
sannan yajata da karfi suka fada kan kujera,
Kallo daya zaka mishi ka gane baya cikin
hayyacin shi,
" plz Afnan dan Allah ki taimaka min wlh ina cikin
tsananin bukatar ki"
Kuka tashigayi na tashin hankali tana rokon Yazid
da yayi hakuri kada ya keta Mata mutuncin ta
amma Ina baxai iya ba shedan yariga yayi mishi
huduba.
Tun tanada karfi tana kokowa dashi tana tureshi
har ta galabaita kasancewar karfi ba guda ba.
Tanaji tana gani Yazid ya rabata da mutuncin ta
Wanda koni kaina marubuciyar saida nayi kuka
ganin halin da Afnan take ciki.

Yazeed ko yaseer


[12/29/2016, 8:36 AM] Ayshart one: Yazeed ko
Yaseer
Nah
Ayshart Farouq
NWA
10-15
Aisha Afnan 'ya ce gun Alh Umar Adam, Wanda
ainihin shi mutumin kano ne, yanada diya uku
Ibrahim, Sagir da Aisha Afnan, matar shi daya
wato Hjy Zainab,
akwai tazarar haihuwa sosai tsakanin yaran su
kuma tun bayan haihuwar Afnan basu sake
samun haihuwa ba shiyasa suka dauke son
duniya suka daura Mata,
tun Afnan tana karama burin mahaifinta tazamo
lawyer, shiyasa kwata kwata bata kula samari
har ta gama secondary school batada wani
saurayi ko wani Wanda take so ba kuma don
babu masoyanba sai dai don wannan ne ra'ayin
ta da na mahaifinta,
Ibrahim kuma ya qare karatun shi na medicine a
jami'ar england yayin da sagir yake karatun
business admin a malesia yayin da Afnan take UG
one a jami'ar bayaro da ke jahar kano tana
karatun law.
Tunda take karatun ta Kawai tasama gaba bata
damu da harakar kowa ba sai ta karatunta,
Tun lokacin da wani guy ya kyalla ido yaganta
yake bibiyar ta amma Ina yayi duk yanda zaiyi
don yaga ya mallaketa amma ya kasa saboda ita
ba irin matannan ne ba da zaka samu lokaci daya
kasanar dasu bukatar ka ba,
Wata Rana ta fita shopping tare da driver sai
motar su tasamu matsala ta tsaya musu kan
hanya ganin lokaci zai kuremata kafin a gyara
yasanya ta yanke shawarar shiga a dai daita,
bayan tashiga shop rite din ne tafara diban kayan
da take so, takai hannunta gurin wani turare
kenan sai aka dauka da sauri ta juya don ganin
KO waye, sai dai kallo daya ta mishi ta sauke
idanuwanta kasa saboda kwarjinin shi da tsabar
haduwar shi, murmushi yayi tare da cewa,
" wannan turaren nawa ne nariga ki ganin shi ki
zabi wani, ko in zabar miki ne? don Sam wannan
ma bai dace dake ba,"
Karo na farko a rayuwata da taji wani namiji ya
burgeta, gyada mishi Kai kawai tayi tana kallon
shi, wani Kala ya dauko Mata ya mika mata ,
karba tayi tare da yi mishi godiya ta wuce abunta
taci gaba da dibar abunda take so,
saida takare kaf sannan taje gurin biyan kuddin,
card dinta ta cire ta mika, ba zato taji ance Ai
anbiya Mata mamaki ne ya kamata ganin kusan
kayan 25k
"toh waye ya biyamin?" ta tambaya nuna Mata
shi akayi yana tsaye sai murmushi yake mata,
daure fuska tayi ta isa kusa dashi,
" malam miye na biyamin kuddi alhalin kuwa ban
saka ba?"
Murmushi yayi tare da cewa,
"Afnan kenan"
Zare idanuwa tayi tana kallon shi jin ya ambaci
sunan ta mika hannu yayi tare da karbar kayan
hannunta " banan ya dace muyi mqgana ba kinga
mutane sunata wucewa a gurin,
Yanda yayi maganar sai taji ya sake burgeta
saboda yasan mutuncin kanshi da darajar diya
macce, sake mishi kayan tayi tare da bin
bayanshi har bakin motar shi,
sanya kayan yayi a motar tare da cewa, "oya
shiga muje "
Girgiza mishi Kai tayi
"a'a bazan shiga motar ka ba tare nake da driver,"
Murmushi yayi
"ai har yanxun bai gyra motar ba"
ya fada yana kallonta,
" Anya kuwa wannan mutum ba aljani ne ba" ta
fada a ranta,
Ganin ba sarki sai allah ne yasanya ta shiga
motar tashi tare da jero mishi tambayoyi " Kai
waye? Kuma a Ina kasanni?"
Murmushi yayi am yazid kuma nasanki da
dadewa ya bata amesa batatare da ya kalleta ba,
" so why did u do all this to me ?" Ta sake
tambayar shi,
Kai tsaye yabata amsa da saboda Ina kaunar ki,
wlh Afnan soyayyar ki ta Dade a cikin raina ban
San ta yanda Zan gaya miki ba saboda naga baki
damu da kowa ba,
Ni sunana Yazid Ahmad Abdulrahman mutane
suna kirana da Ahmad Y Abdulrahman Ina
masters ne a bayaro university anana na sanki
faculty dinmu daya dake I hope wannan ya
gamsar da ke,?"
Ita dai Afnan kasa cewa komai ta yi saboda
mamakin shi da yakamata ganin har saida
yakawota bakin motarsu da ake gyara,
" idan baxaki damuba Ina son ki bani number ki
ko don murika zumunci,"
Ba musu sukayi musayar number, toh tun daga
ranar suka fara waya kuma suna haduwa a
school tun dai Afnan tana dari dari fashi har ta
daina ta saki jikinta dashi soyayya mai tsanani
tashiga tsakanin su,
Nan ta fayyace mai ra'ayin mahaifinta akanta
inda Shima akayi sa'a iyayen shi sunada wannan
ra'ayin duk da bai Kai irin na mahaifinta ba, haka
yasa Yazid ya daukarma alkawarin aure duk wuya
duk rintsi..
[12/29/2016, 8:36 AM] Ayshart one: Yazeed ko
Yaseer
Nah
Ayshart Farouq
NWA
15-20
Da sauri ta Afnan ta is a gida gabanta sai
faduwa yake ganin motar mahaifinta, Mai aikinsu
taxi Karo da ita a falo cikin faduwar gaba tace, "
momy fah?"
Salah Mai aiki tace," tana sama gurin Alhaji,"
Dakinta ta wuce jikinta duk ya mutu tayi zaune
tare da rafka uban tagumi Allah Allah take tana
addu'a Allah yasa baima momynta fada ba, tana
cikin hakane taji wayar mimynta ta sake shigowa,
da Sauri ta dauka " momy na dawo tun dazu Ina
daki"
Can bangaren aka amsa da cewa, " Afnan kizo
dadyn Ku na neman ki,"
Batare da bata lokaci ba ta nufi part din
mahaifinta cikin faduwar gaba don har ga Allah
ta tsane kiran mahaifin nata duk da tasan baima
fiye yimata tsanani ba akan sauran yayunta.
Da sallama ta shiga dakin tare da gaida iyayenta,
cikin fari'a Abba ya ce, " zo nan uwata" murmushi
Afnan ta Saki ganin ba wata matsala,
Can ta matsa kusa da abbanta yayin da wayarta
tayi Kara, da sauri mahaifinta ya kalleta tare da
mika hannu ya karbi wayan don ganin ko waye
yake kiranta,
Cikin tashin hanakali Afnan ta mika mishi wayar
ganin sunan dake rubuce wato maryam2 ,
Ganin sunan ne yasanya yamika Mata wayar tare
da cewa, " dauki wayar tukun,
Hannunta har rawa yake gurin karbar wayar,
kafin tayi wani abu har Call din ya tsinke, ajiyar
zuciya tayi har saida abban Nata ya kalleta,
Kafin suce komai wayar ta sake daukan ruri, a
hanakali ta Kara wayar a kunne " assalamu
alaikum" can bangaren aka amsa da "my princess
da fatar kin isa gida lfy", marar gaskiya Ko a
ruwa sai yayi jibi duk a.c dake dakin bai Hana
Afnan yin zufa ba don ganin take tamkar
mahaifinta najin abunda Yazid ke fadi ,
A sanyaye tace, " eh wlh maryam nazo ban
sameki ba , ok to sai mun hadu islamiyar gobe,"
tayi saurin datse wayar tare da mikawa Abbanta
wayar,
Cikin murmushi ya karba, sai da ya duba
contacts dinta kaf duk tana zaune tana kallon
shi, wata kwalla Ce ta zubo Mata wadda batasan
lokacin da ta zubo ba.
Momy dai zaune kawai take tana Lura da halin da
diyar tata take ciki, nan take duk tausayin ta ya
kamata yayin da cikin ranta take tir da hali irin na
mijinta da ya kasa gane halin da rayuwa take ciki
a wannan zamani,
Kasa hakura tayi saida tayi magana
" amma dai fisailillahi alhaji abunda kakewa Afnan
Sam bai dace ba kaine ka haifeta amma ace ka
kasa yadda da ita wannan wace irin rayuwa ce,
Dagowa yayi ya kalleta fuskarshi tamke,
" bana son irin abunda kike mun zainab ni Ina
hango abunda baki hango ba, kun matsa abata
waya na bata waya don haka dole ne a gareni
matsayina na mahaifinta in Lura da abunda take
da wayar don bana so Allah ya kamani da wani
laifi akan tarbiyar Afnan gobe kiyama, don haka
idan kinji kina iya taimaka min mu tarbiyantar da
ita walillahil hamdu idan kuma kinji baki iyawa
kuwa kada ki sake min magana akan abunda
nake ganin shine dai dai."
Cikin bacin rai momy tace, "ai wannan abun da
kake ba shine tarbiya ba, tarbiya duk bai wuce ka
aurar da ita ba "
Daga Mata hannu yayi " kinfi kowa sanin cewa ni
mutum ne wanda yake so yaga Dan Adam ya
dogara da kanshi don haka maganar aure ba
matsala bace, idan lokaci yayi ni da kaina Zan
zabo Mata mijin da ya dace da rayuwarta,"
Afnan najin wannan maganar Bata San lokacin da
ta fashe da kuka ba Wanda saida yabaiwa iyayen
nata mamaki dukan su ,
Da sauri Abba ya dubeta " miye haka Afnan? Mi
kekewa kuka ne?
Cikin bacin rai momy tace, " ai dole tayi kuka
tunda taji kana nema ka tauye Mata hakki,
wallahi alhaji kaji tsoron Allah kasani yanda
mukeda hakki akan yaranmu haka suma suke da
hakki a kan mu,"
Jikin Abba yayi matukar sanyi baice komai ba ya
mikawa Afnan wayarta tare da cewa ,
" tashi kije daki Afnan yi hakuri share hawayen ki,
jeki Zan sake nemanki ,"
Jikin Afnan sanyi kalau ta tashi taje daki da
tunani da yawa a zuciyarta ,
Number maryam2 ta lalubo wato Yazeed dinta,
fira suka shigayi sosai tamkar za su cinye junan
so saboda so da kauna, basu sukayi sallama ba
saida aka fara kiran sallahr magriba..
Ayshart one
[12/29/2016, 8:36 AM] Ayshart one: Yazeed ko
Yaseer
Nah
Ayshart Farouq
NWA
20-25
Bayan sati biyu da faruwar haka Afnan suka
koma makaranta wannan karon komawa hutun ya
Mata dadi don kusan kullun tana tare da Yazeed
dinta karatun ma yanzu tafara ja baya dashi don
wani lokaci ko attending lectures batayi tana can
gurin yazeed suna soyewa haka kuma idan
tadawo gida matukar tana daki to kuwa suna
manne a waya,
Afnan! Afnan!" Taji muryar yayanta sagir yana
kwala mata kira,
Harararsa tayi , " miye ne" tana kwance kan gado
rungume da wayarta tana waya da Yazeed,
hankalinta kwance saboda ba kowa zai fahimce
waya takeyi ba amma duniya taki jinin tana waya
dashi a katseta ,
Ganin hararar da take ta zuba mishi ne yasanya
sagir din karasowa cikin dakin,
" ni kike harara?, Allah Zan buge idanuwan nan"
Turo baki tayi " to miye ne na kwalamin Kira
haka kaman kaban ajiya ne"
Tsaki yaja " to Abba ne ya aikoni in kiraki, idan
kuma bazakije ba sai inje in fada masa kina waya
bakida lokacin amsa kiransa",
Zaro idanuwa tayi "Allah gaya sagir ba waya
nakeyi ba waka ce nake sha kada kamin sharri
wlh bazan sake hararanka ba kayi hakuri Dan
Allah kace, Ina zuwa"
"Kyat" yayi kyafci tare da banka Mata harara, "
yace, " kinyi sa'a wlh da kinga sharri,"
Nan ya fice ita kuma ta mike da sauri,
Ta bangaren Yazeed kuwa sai tsokanarta yakeyi
da yake headphone ne a kunnen ta,
" kicewa Abba kina biyayya Wa miji ne kina
faranta masa rai kina masa fira Mai dadi yana jin
muryarki Mai dadi tana ratsa jikinsa kina samun
lada,"
Dariya Afnan din tayi tare da cewa,
"Yazeed kenan!, kwarai kuwa Zan gaya mishi idan
yazo min fada har Kai sai a tattara a hada"
Shima dariya yayi "ba komai ai kin San dama
dadi da wuya munyi alkawarin rabashi nida ke,"
Murmushi tayi tamkar yana ganinta, " Zan dauki
wuyar ka dauki dadin"
"_a'a ni Zan dauki wuya ke ki dauki dadin"
" ni dai a'a" ta fada cikin muryar shagwaba,
A kasalance yace, "kin ganki ko? kin Fara kashe
min jiki da shagwabar nan taki ko? Yanzun
tunanin ki sai ya fitine ni ya hanani sakat,"
Dariya tayi " ai haka nake so tunanina kadai
yafitine zuciyarka "
"Afnan" ta sake jin muryar mahaifiyarta, da sauri
ta katse wayar ta fita da gudu, tace,
" gani nan zuwa momy ina toilet ne "
" toh maza kiyi sauri Abban Ku na son magana
dake tun dazu"
Ta karba da " toh momy"
Nan da nan ta nufe falon nasa zuciyarta cike da
tunanin KO wane Kira ne yake Mata ?,
Ganin Ibrahim da sagir ne da tayi da kuma
mahaifan nata yasanya gabanta yashiga faduwa
dole ne tasan akwai maganar da Abbanta zai
mata.
Aysh

Yazeed ko yaseer

           Yazeed ko yaseer
                  Nah
        Ayshart Farouq
                 
                 NWA
   

              5_10

Dariya Yazeed din yayi tare da lakuce Mata hanci " sarkin tsoro to wasa nakeyi",

Afnan tayi ajiyar zuciya tare da cewa "toh bana son irin wannan wasar ka daina plz"

" Allah ya huce ran gimbiya  nadaina"

Yanda yayi maganar saida yabata dariya kasancewar shi mutum ne Mai barkwanci,

Shima dariyar yayi tare da cewa,
" wallahi Afnan Ina son aure "

Gaskiya ya bata tausayi yanda yayi maganar sai dai tafishi zama abun tausayi kasancewar cewa ita mace ce tanada rauni sosai hardai wannan zamani da muke ciki a yanzu,

Muryarshi ce ta katse Mata tunanin ta,  "  Afnan nasan bakya jin yanda nakji ko?" Ya fada tare da zuba Mata idanuwa,

Cikin muryar tausayi tace, " ko inaji ya muka iya?  dole mu hakura da abunda iyayen mu suke so shekara biyu ai kaman gobe ne,"

" ai bama tani ba ni, ke nake dubi tunda kema ra'ayin mahaifin ki kenan kiyi karatu Mai zurfi kinga kuwa ba shekara biyu ba akwai sauran lokaci da yawa tunda na tabbatar da cewa ko mahaifin ki zai miki aure sai kin Kai UG 4 ko five  gashi yanxun kike UG 1"

Gabanta ne ya Fadi tuna maganar mahaifinta, lokaci daya damuwarta ta karu harma da guntuwar kwallarta
Cikin sanyin jiki ta dubeshi,
" toh ya kenan? Nasan bazaka iya jirana ba ko?"

Murmushi ya kakalo " haba ya zakice haka? Zan jiraki mana ko shekara goma ne kuwa na miki alkawari"

Wani sanyi taji a ranta tare da Kara jin sonshi yana shigarta ta KO ina,
Cikin ranta kuwa haushin akida takeji irin ta mahaifinta,

Hannunta ya Dan Kama tare da murza yatsunta, " me kike tunani ne?"
 
Da sauri ta kwace hannunta tare da hararan shi, " miye haka? bana son irin haka fah"

Kunnuwan shi ya Kama tare da marairaice fuska " am sorry plz"

Wayarta ce tayi ringing da sauri ta duba ganin mahaifiyarta ne yasanya taji  gabanta ya fadi,
Cikin  tsoro ta dube Yazeed dake kallonta,
Tace, " nashiga uku momy ce"

" dauka kice Mata kina hanya" ya fada cikin  rada,

Cikin ladabi ta dauki wayar,   "momy Ina hanyar dawowa," tafada tere da katse wayar ,

A gurguje sukayi sallama da Yazeed  duk da cewa ba haka yaso ba ita kanta ma ba haka taso ba sai dai don ba yanda suka iya ne, haka suka rabu cikin kaunar junan su tare da kewa Mai tsanani,
Kasancewar satinsu uku basu hadu ba ta dalilin Hutun da Afnan din keyi na makaranta.

Ayshart one

Yazeed ko yaseer

              Yazeed ko Yaseer
                         
                         Nah
       
                 Ayshart Farouq

                           NWA

                       1_5

         Zaune take kan sallayarta ta idar da sallar la'asar tana istigfari, mace ce 'yar kimanin shekara  arba'in da biyu zuwa da uku, amma Sam batayi Kama da shekarunta ba saboda irin kyaun jikin da Allah ya Mata da kuma kasancewar ta 'yar Hutu, idan ance ka fadi shekarunta zaka iya  rantsewa 'yar talatin ce,
Kyakkyawa ce mai cikar mutunci da kamala,

     Wata kyakkyawar yarinya naga tafito cikin shirinta da alama fita zatayi don sanye take da hijab Mai hannu iya  gwiwa, hannuwanta riqe da yar post dinta kalar takalminta ko ba'a fada ba kasan cewa diyar hajiya zainab ce saboda tsantsar kamar da sukayi duk da cewa yarinyar bazata wuce shekara  goma shatakwas ba.

   Gurfanawa tayi gaban mahaifiyar tata tana murmushi tare da cewa,
" momy naga kina ta kallo na " ta fada cikin shagwaba,

" ba dole in kalleki ba naga kinci uban ado haka kuma kinsan yau ba islamiya"

b'ata fuska tayi , " haba momy nafa gaya miki ina so inje gurin kawata maryam in karbo wani littafi da nake so in koya gurin malaminmu"

Cikin fada fada momyn tata take magana,
" kin San dai mahaifinki baya son irin wannan yawon ko ? Ko so kike yadawo bai ganki ba  ya hauni da fada? Gskiya abunda kike mun Afnan Sam ba na son shi kin fi kowa sanin halin mahaifin ki amma ke Sam ba kya gudun abunda kanje ya dawo,"

Cikin ladabi da girmamawa Afnan take magana " Dan Allah momy kiyi hakuri insha allahu Abba bazai dawo yasame bana nan ba amma idan har bakya son fitar na hakura sai wani lokaci sai inje in karbo"
Ta karashe maganar tare da mikewa idanuwanta cike da kwalla ta juya zata koma,

Cikin sanyin ta ta kirata da " Afnan kije amma kada ki dade kinji autar momy plz kada kiyi kuka ki b'ata kwalliyar ki",

Cikin murna da jin dadi Afnan tayi godiya sannan ta juya ta fita tana murna.

     Ahankali ta ke tafiya saida tayi nisa da gida kadan sannan ta bude post dinta ta fidda wayarta kusan 12 miss call ta gani kasancewar wayar silent take,
Murmushi tayi lokaci daya ganin wani kiran ya shigo da number da akayi saving da maryam2,

Cikin muryarta Mai dadin sauraro  take karba wayar, " dan Allah kayi hakuri gani nan na kusa karasowa kasan fitar saida dubaru, OK toh sai na karaso ta fada tare da kashe wayar ,

Tafiyarta takeyi cike da nutsuwa har takai bakin wata mota kirar prado jib baka wulik sai sheki take,

Murmushi suka sakarwa junan su lokacin da idanuwan su suka sarke guru daya ,

    Ahankali ya bude motar ya fito wanda lokacin da naganshi saida nakusa fita hayyaci na saboda tsananin haduwar shi wadda duk yanda ka Kai gurin kushe mutum bazaka taba kushe shi ba  don bazaka taba iya cewa ga munin shi ba,

Cikin fari'ar shi yake cewa, " amma fah gskiya ya kamata ace nayi fishi da ke my princess sai dai kuma kash bazan iya ba,
        
Murmushi Afnan tayi irin Wanda ke karamata kyau da annuri ,

" ki daina min irin wannan murmushin yana kara zuzutar da ni, wani murmushin ta sakeyi Wanda yafi na farko kayatarwa,

" kaifah YAZID akwaika da abun dariya wlh" ta fada tana duban shi

" Allah ko princess?" Ya fada shima yana Mata wani irin shu'umammen kallo tare da cewa,
" kin San wani Abu?"
Tace ," sai ka fada"

Kanshi ya dan sosa " Allah KO wace irin shiga kikayi kyau kike yi"

Wannan Karon tuntsirewa Afnan  tayi da dariya " Allah yazeed ka cika abun dariya nufah duk daukana abun kwarai zaka fada"

Shima cikin dariya yace, " au wannan ba abun kwarai ne ba kena?"

Murmushi tayi tare da cewa,
" toh yanzu ya ake ciki ne? Kasan karya na zubawa mom  tace kada nadade banaso nabata Mata rai gobe ta hanani,

" haka ne kam" ya fada tare da sosa keya " gashi kuwa ma naso ki rakani wani guri"

Zaro idanuwa tayi tare da daure fuska "amma dai wasa kakeyi ko?"


 
Ayashart one